Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin masu saurare kan shirin sake rubuta tarihin Nijar

Informações:

Sinopsis

Gwmanatin Jamhuriyar Nijar ta kafa kwamitin ƙwararru wanda ta ɗora wa alhakin sake rubuta tarihin ƙasar, lura da cewa yawancin abubuwan da ake faɗa game da ƙasar a halin yanzu Turanwan mulkin mallaka ne suka rubuta su. Shin ko meye muhimmanci rubuta sabon tarihin wanda aka ɗanka wa masana ƴan ƙasar a maimakon wanda aka gada daga ƴan mulkin mallaka? Anya abu ne mai yiyuwa a iya sauya bayanan da ke rubuce a game da ƙasar waɗanda tuni suka karaɗe duniya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...