Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar neman korar 'yan Najeriya daga Ghana

Informações:

Sinopsis

A ƴan kwanakin nan an samu ɓarkewar zanga-zangar a Ghana, inda ƴan ƙasar ke zargin ƴan Najeriya da ke can da aikata laifuka kisan gilla da karuwanci, lamarin da ya sa masu zanga-zangar neman a koresu daga ƙasarsu. Haka nan masu zanga-zangar sun yi ikirarin cewa ƴan kasuwan Najeriya  sun mamaye musu kasuwanni tare da karya dokokin kasuwanci a ƙasar. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...