Sinopsis
Shirin Lafiya yana tattaunawa da likitoci da mahukunta a game da kiyon lafiyar jamaa, Sanin sabbin magunguna da binciken kimiya ya samar. Ana gabatar da shirin a ranar Littinin da hantsi, tare da maimaici a ranar Talata da yamma.
Episodios
-
Matsalolin da yawan shan suga ke haifarwa jikin mutum a lokacin da ya girma
02/06/2025 Duración: 09minShirin Lafiya Jari Ce a wannan makon shirin ya mayar da hankali kan yadda wani bincike ke gano cewa yawan shan suger ko kuma sikari a lokutan ƙuriciya na taka muhimmiyar rawa wajen haddasawa mutum ciwon suga a lokacin girma. Wannan cuta ta suga ko kuma Diebetes na cikin jerin cutukan da ke barazana ga rayukan ɗimbin mutane musamman a sassan Najeriya da tuni cutar ta fara zama ruwan dare mai gama duniya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu............
-
Sharhi kan ƙiba fiye da ƙima da ke baraza ga matasan Afirka
26/05/2025 Duración: 10minShirin 'Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan hasashen da wata ƙungiya ta yi cewar nan da shekarar 2025 raɓin al'ummar Afirka masamman matasa za su fuskanci cutar ƙibar da ta wuce ƙima ko Obesity a turance.
-
Ƙaruwa masu kamuwa da cutar tarin fuka a sassan Jamhuriyar Nijar
19/05/2025 Duración: 09minShirin namu na wannan makon zai mayar da hankali ne kan ƙaruwar mutanen da ke kamauwa da cutar babban tari, ko kuma tarin fuka, ko kuma TB a sassan Jamhuriyar Nijar, lamarin da ke zuwa a lokacin da ake fuskantar ƙarancin agajin magangunan yaƙi da wannan cuta. Wanmnan cuta na sahun daɗaɗɗun cutuka masu yaɗuwa, waɗanda wani kan iya goga wa wani.Abin da ya sa ya zama wajibi a rika wayar da kan al'umma akan hanyoyin kariya daga ita.
-
Yadda aka sake samun ɓullar cutar Polio a Najeriya
12/05/2025 Duración: 10minShirin Lafiya jari ce a wannan makon ya yi duba na musamman game da dawowar cutar Polio a Najeriya, cutar da alamu ke nuna nasarar yaƙarta ke yiwa ƙasar kwan gaba kwan baya, lura da yadda a lokuta da dama ake sake ganin ɓullarta bayan nasarar kawar da ita, kodayake ƙwararru sun ce wadda ta ɓulla a wannan karon ba wadda aka saba gani ba ce kuma bata kai waɗanda suka gabace ta illa ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu............