Al'adun Gargajiya

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 4:00:59
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

Kawo aladu na zamani da wadanda suka shude daga sassan kasashen duniya domin mai sauraro ya san cewa, duniyarmu tana da girma da yawan jamaa masu aladu daban-dabam.  Akwai kuma Shirin al'adunmu na musamman na karshen mako da mu ke gabatarwa a ranakun Asabar da lahadi.

Episodios

  • Yadda aka zamanantar da al'adar 'Dalilin Aure' a ƙasar Hausa

    22/04/2025 Duración: 10min

    A yau shirin zai mayar da hankali ne akan al'adar 'Dalilin Aure' a ƙasar Hausa da yadda aka zamanantar da ita.A baya masu 'Dalilin Aure' a boye suke a cikin al'umma, sai dai yanzu a iya cewa zamani riga, domin kuwa za ka iske sun bude ofisoshi tare da sanya alamar cewa anan fa Dalilin aure ake. 

  • Al'adar dalilin aure ta sauya sabon salo tsakanin al'ummar Hausawa

    15/04/2025 Duración: 09min

    Shirin al'adunmu na gado tare da Abdoulaye Issa a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adar nan ta dalilin aure, guda cikin al'adun Hausawa da aka shafe tsawon lokaci ana amfani da ita da nufin haɗin aure walau tsakanin ƴammata da Samari ko kuma Zawara. Kamar yadda kusan kowanne lamari ke tafiya da zamani itama al'adar ta juye, ta yadda ta koma cikakkiyar sana'a da wasu ɗaiɗaikun mutane ke da gogewa akanta, har ta kai ga ake buɗe ofisoshi don gudanar da ita.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.

  • Al'adar tashe na fuskantar barazanar gushewa a ƙasar Hausa

    01/04/2025 Duración: 09min

    Kamar yadda aka saba, shirin yakan yi dduba ne akan al'adun al'ummar Hausawa da sauran su, waɗanda suka gushe ko kuma ake ganin wanzuwan su a yanzu.Al'adar tashe dai na daga cikin al'adun da aka fara ganin yaɗuwarsu a ƙasar Hausa tun a ƙarni na 16, al'ada ce da ta ƙunshi wasannin barkwanci, waɗanda ake gudanar da su da zarar a kammala azumin goman farko na watan Ramadana. Sai dai wannan al'ada ta fara gushewa. Ko menene dalilin haka? Abin da shirin wannan makon zai yi nazari a kai kenan.

  • Aikin ƙwado da linzami na fuskantar barazanar disashewa

    25/03/2025 Duración: 10min

    shirin Al'adun Mu na Gado na wanan makon tareda Abdoulaye Issa ya  leka Jihar  Maradin Jamhuriyar Nijar inda al’adar aikin kwado da lizzami da aka share shekaru ana yin sa da hannu ke fuskantar barazanar samun babban koma baya sakamakon wasu sabbin na’urori ko teloli na zamani da aka samu masu aiki da Computer wadanda ke zuba wannan aiki ga riguna cikin gaggawa. Ku shiga cikin alamar sauti domin sauraron shirin....

página 2 de 2