Sinopsis
Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-dabam a duniya, tare da nazari ga irin ci gaban da aka cim ma wajen binciken kimiya da fasaha da ke naman saukakawa Danadam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Biladam. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe.
Episodios
-
Ƙalubalen da suka dabibaye harshen Hausa ta fuskar rubutu - Kashi na 1
15/04/2025 Duración: 09minShirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan makon shirin ya sauya salo zuwa mai dogon zango ta yadda zai tattauna da masu ruwa da tsaki a kan bunƙasar harshen Hausa da matsalolin da ya ke fuskanta da dalilan da suka haifar da matsalolin, da dai sauran muhimman batutuwa da suka shafi harshen na Hausa. Harshen Hausa, harshe ne da yake da tsohon tarihi wanda ya shafe ɗaruruwan shekaru ana magana da shi, wanda alƙaluma suka tabbatar da cewar zuwa yanzu miliyoyin mutane ne ke magana da harshen a sassan duniya.Wani rahoto da aka wallafa a shekarun baya bayan nan ya nuna cewar a halin yanzu Harshen Hausa ne Harshe na 11 da aka fi amfani da shi a duniya, zalika an yi ƙiyasin cewar mutane miliyan 150 ne ke magana da shi a sassan Duniya.Masana na kallon waɗaccan alƙaluma a matsayin dallilan da suka sanya harshen na Hausa yin shaharar ta kai ya yi gogayya da dukkanin manyan harsunan duniya, lura da yadda harshen ke da yalwar kalmomi da za a iya sarrafa su gami da bayyana kowanne irin tunani da su, walau
-
Yadda yaran 'yan makarantun firamare suka koma haƙar ma'adanai a Najeriya
08/04/2025 Duración: 10minShirin na wannan mako ya duba yadda ƙananan yara 'yan makarantun firamare suka karatu domin aikin haƙar ma'adanai saboda cimma bukatun yau da kullum a jihar Bauchin Najeriya. A latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
-
Yadda ɗalibai a Bauchi ke watsi da karatu don shiga aikin tonon ma'adinai
01/04/2025 Duración: 10minShirin wannan makon zai yi dubi ne akan yadda ɗalibai a jihar Bauchi ke yin watsi da karatu don shiga aikin tonon ma'adinai.Jihar Bauchi, ta yi ƙaurin suna a baya a matsayin wadda ke sahun gaba wajen yawan yaran da suka yi watsi da makarantunsu tare da rungumar harkar tonon ma’adinai don samun dogaro da kai.Dalili ke nan da fiye da rabin daliban wasu makarantun firamare a jihar, suka bar zuwa makaranta inda suka karkatar da hankali kan harka haƙon ma’adanan.
-
Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin ɗaukar nauyin karatun ƴaƴa mata zuwa PHD
25/03/2025 Duración: 09minShirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya maida hankali ne kan shirin da gwamnatin jihar Jigawa ta ƙaddamar, na ɗaukar nauyin karatun ‘ya’ya mata daga Firamaren har zuwa karatun Digirin Digirgir, shirin da ta ce tana fatan zai zaburar da ƙarin mata da iyayensu wajen duƙufa neman ilimi, ba tare da fargabar fuskantar ƙalubale na rashin ƙarfi ta fuskar tattalin arziƙi ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare Nura Ado Suleiman.........